26 Afrilu 2025
Sojojin Indiya da na Pakistan sun yi musayar harbe-harbe a daren jiya a kan layin iyaka da ya raba ƙasashen biyu a yankin Kashmir da ake taƙaddama a kai, a karo na biyu a jere, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito, yana ambato rundunar sojin Indiya.
Rundunar sojin Indiya ta ce an yi harbe-harben "na ba gaira ba dalili" daga wurare da dama na sojojin Pakistan "a tsawon layin iyaka a Kashmir" daga daren Asabar zuwa wayewar gari.
"Sojojin Indiya sun mayar da martani yadda ya kamata da ƙananan makamai," in ji sanarwar. "Ba a samu rahoton asarar rai ba."