SIYASA
1 minti karatu
Turkiyya ta yi watsi da zargin kai wa Pakistan makamai
Sashen Sadarwa na Turkiyya ya ce jirgin dakon kayan ya sauka a Pakistan ne don shan mai, yana mai watsi da ikirarin wai Ankara ta aika da jiragen sama shida ɗauke da makamai zuwa Islamabad.
Turkiyya ta yi watsi da zargin kai wa Pakistan makamai
Sashen Sadarwa na Turkiyya na yaki da yada labaran karya: TRT World / TRT World
28 Afrilu 2025

Sashen Sadarwa na Turkiyya ya musanta rahotannin kafafen yaɗa labarai da ke cewa Ankara ta aike da jiragen sama shida ɗauke da makamai zuwa Pakistan.

A wata sanarwa a ranar Litinin ta shafin X, Cibiyar Yaƙi da yaɗa Labaran Ƙarya ta Sashen ta ce ikirarin, wanda ya ɓulla a wasu kafafen yaɗa labarai, ba gaskiya ba ne.

“Jirgin ɗaukar kaya daga Turkiyya ya sauka a Pakistan don ƙara mai. Bayan haka, jirgin ya tafi zuwa inda ya nufa.”

Sanarwar ta kara da cewa “Bai kamata a yi amfani da rahotannin jita-jita na waɗansu mutane ko hukumomi ba da ba su da hurumi.”

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us