logo
hausa
Labaranmu Na Yau, 6 ga watan Mayun 2025
04:06
Labaranmu Na Yau, 6 ga watan Mayun 2025
Gwamnatin jihar Borno za ta rufe sansanin 'yan gudun hijira saboda karuwar munanan ayyuka sannan za a ji cewa MDD ta yi gargadin cewa Isra'ila na amfani da ruwa wajen lalata al'ummar Gaza

Gwamnan jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nijeriya Babagana Umara Zulum, ya bayyana shirin sake tsugunar da iyalai 6,000 daga sansanin ‘yan gudun hijira na Muna da ke Maiduguri, saboda karuwar miyagun ayyuka da suka hada da karuwanci da cin zarafin yara da dai sauransu.

A ziyarar da ya kai sansanin, wanda ke dauke da iyalai kusan 11,000 da suka rasa matsugunansu, Zulum ya jaddada cewa sake musu matsugunan na da matukar muhimmanci wajen dakile munanan dabi'u da kuma samun zaman lafiya mai dorewa.

Ya ma nanata cewa mayar da jama’a zuwa yankunansu shi ne mabudin murkushe mayakan kungiyar Boko Haram.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us